Kamfanin Dillancin Labaran ƙasa da ƙasa na Ahlul-Baiti (ABNA) ya habarta cewa: Jaridar Ibrananci "Jerusalem Post" ta nakalto wata majiyar tsaro cewa Hizbullah ta kai mafi ƙarfin harin ta na jirage marasa matuki a jiya kan arewacin Falasdinu da aka mamaye.
Wannan majiya ta bayyana cewa a yayin harin jiragen marasa matuki na Hizbullah, jami'an Sahayoniya biyu sun jikkata, kuma a wani hari na daban an samu gobara a wani sansanin soji a arewacin Falasdinu da aka mamaye.
Hizbullah kimanin awa daya bayan guguwar farko ta hare-hare, ta harba wasu jirage marasa matuki da dama zuwa ga wannan sansani a arewacin Falasdinu da aka mamaye.
Majiyar tsaro ta kuma jaddada cewa Hizbullah a jiya ta aiwatar da wani hari na jirage marasa matuki wanda aka tsara, wanda a fannin faɗi da yadda aka aiwatar da shi, shi ne hari na farko irinsa a kan arewacin Falasdinu da aka mamaye.
Your Comment